Lada Don Adalci na ba da tayin lada da ya kai dalar Amurka miliyan don bayanai kan harin da aka kai kan rukunin gidaje a babban birnin Saudiyya a shekarar 2003. A ranar 12 ga watan Mayun 2003, mahara aƙalla 15 ne suka kai wa rukunin gidajen hari a wata unguwa da ke birnin Riyadh. Bayan sun haura shingen tsaro, maharan sun tashi bam-baman da suka ɗana a mota, inda suka kashe mutum 35 har da Amurkawa tara, suka raunata wasu kusan 200. Wuraren da aka kai harin gida ne ga Turawan Yama da dama, musamman Amurkawa da ‘yan Birtaniya. Al-Qa’ida ce ta shirya tare da aiwatar da harin.
