Mohamoud Abdi Aden

Afirka – Kudu da Hamadar Sahara

Lada

Har zuwa dalar Amurka miliyan 10

Ba da gudunmawarka.

Shirin Lada Don Adalci na ba da tayin ladan da ya kai dala miliyan 10 don neman bayanai kan Mohamoud Abdi Aden, jagoran al-Shabaab da ya taimaka wajen kai hari kan otel ɗin DusitD2 ranar 15 ga watan Janairun 2019 a Nairobi, Kenya. Yayin harin, mayaƙan al-Shabaab ɗauke da manyan makamai da gurneti da sauran abubuwan fashewa suka kai hari a cibiyar kasuwanci ta DusitD2, wanda ya ƙunshi rukunin gidaje shida mai ɗauke da shaguna da ofisoshi da kuma otel. Aƙalla mutum 21 aka kashe a harin, cikinsu har da Ba’amurke.

A ranar 17 ga watan Oktoban 2022, Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ayyana Aden a matsayin Ɗan Ta’adda na Duniya a ƙarƙashin Umarnin Shugaban Ƙasa na 13224, wanda aka yi wa kwaskwarima.

 

Skip to content