Hari kan ginin otel ɗin DusitD2 da ke Nairobi, Kenya

Afirka – Kudu da Hamadar Sahara

Lada

Up to $10 Million

Ba da gudunmawarka.

Shirin Lada Don Adalci na ba da tayin ladan da ya kai dala miliyan 10 don neman bayanai kan Mohamoud Abdi Aden, da duk wani da ke da hannu a harin dqa al-Shabaab ta kai a 2019 kan otle ɗin DusitD2 a Nairobin Kenya. Da tsakar 15 ga watan Janairun 2019, mayaƙan al-Shabaab ɗauke da manyan makamai da gurneti da sauran abubuwan fashewa suka kai hari a cibiyar kasuwanci ta DusitD2, wanda ya ƙunshi rrukunin gidaje shida mai ɗauke da shaguna da ofisoshi da kuma otel. Aƙalla mutum 21 ne, ciki har da Ba’murke, aka kashe a harin. Al-Shabaab – mai alaƙa da ƙungiyar ta’addanci ta al-Ƙa’ida – ta dinga nuna harin kai-tsaye a shafinta na Shahada News Agency kuma ta ba da sanarwa cewa shugaban al-Ƙa’ida na lokacin Ayman Zawahiri ne ya ba da umarnin kai harin.

Wani jagoran al-Shabaab mai suna Aden ne ya shirya harin na Janairun 2019. A ranar 17 ga watan Oktoban 2022, Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ayyana shi a matsayin Ɗan Ta’adda na Duniya a ƙarƙashin Umarnin Shugaban Ƙasa na 13224, wanda aka yi wa kwaskwarima.

Al-Shabaab ce ke da alhakin kai hare-haren ta’addanci da dama a Kenya, da Somaliya, da kuma maƙwabtansu tare da kashe dubban mutane, ciki har da Amurkawa. Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ayyana al-Shabaab a matsayin Ƙungiyar Ta’addanci ta Duniya a watan Maris na 2008. A watan Afrilun 2010, Kwamatin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNSC) ya sake ayyana al-Shabaab a ƙarƙashin yarjejeniya ta 1844 (2008).

Skip to content